DAKARUN SOJOJIN SAMA NA NAJERIYA SUN CETO WASU MUTANE DA AKA YI GARKUWA DA SU A JAHAR KADUNA.

Dakarun Sojin saman Najeriya (NAF) na musamman a yau, 12 ga watan Janairu, 2022, sun ceto mutane 26 da aka yi garkuwa da su a yayin da suke sintiri a kan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna.

Aikin ceton ya faru ne a lokacin da dakarun na musamman suka ci karo da wasu motoci guda 5 babu kowa a cikin su kuma kofofin su a bude a Anguwar Yako, lamarin da ke nuni da cewa mutanen ciki an sace su ne da kuma yiwuwar yin garkuwa da su.

Dakarun,sun fara gano wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su sun fito kwatsam daga cikin jeji. Bayan bincike mai zurfi a cikin yankin, an ceto jimillar mutane 26 da abin ya shafa.

Wasu da aka ceto

Da ake yi wa wadanda abin ya shafa tambayoyi daga Birnin Gwari zuwa wurare daban-daban da suka hada da Kaduna, Minna da Kano, sun bayyana cewa, a yayin da suke cikin tafiya, sai ga wasu gungun ‘yan bindiga da dama da suka fito daga cikin jeji daga wurare daban-daban da ke kan hanyar, suka kewaye motocinsu.

Duk da namijin kokarin da rundunar ta yi, maharan sun gudu da wasu mutanen cikin daji.

Wasu da aka ceto tare da sojojin sama.

Rundunar sojin saman, ta tsawaita ayyukan ta a yankin tare da fatan ceto sauran wadanda aka yi garkuwa da su yayin da aka kai wadanda aka ceto zuwa Asibitin sojojin smam na Kaduna domin duba lafiyarsu.

EFCC Ta Kama Wani da ake zargin da karkatar da N6m da aka wakilta shi don sayan shinkafa a Kaduna.

Suleiman Aliyu

Wanda ake karar, a wani lokaci a shekarar 2019 ya karbi tan 49 na shinkafa wanda kudinsa ya kai N6, 000,000.00 daga hannun wanda ya kai karar amma ya kasa biya bayan wa’adin da aka amince da shi.

A tuhume-tuhumen, alkali ya ce, “Wani lokaci a cikin Janairu, 2019, kai Suleiman Aliyu, a Kaduna da ke karkashin ikon wannan kotu mai girma, ka yi rashin gaskiya ko kuma ka yi amfani da kudinka N 6,000,000.00 (Naira Miliyan Shida) mallakar Ibrahim Hassan. don samar da shinkafa ton 49 na sarrafa shi wanda kuka canza ba tare da izininsa ba kuma da nufin hana shi kuɗin da aka ambata na dindindin kuma kuka aikata laifin da ya saba wa sashe na 293 na kundin laifuffuka na jihar Kaduna, 2017, kuma mai hukunci a sashe na 294 na doka daya”.

Wanda ake tuhumar ya musanta aikata laifin. Dangane da rokonsa, Lauyan masu kara, E.K Garba ya bukaci kotun da ta sanya ranar da za a fara shari’ar. Amma lauyan wanda ake kara, Sanusi S.G ya bukaci kotu da ta shigar da wanda yake karewa beli.

Suleiman Aliyu

Mai shari’a Khobo ya bayar da belin wanda ake kara a kan kudi N 3,000,000.00 da kuma wanda zai tsaya masa a daidai wannan adadi, wanda dole ne ya kasance mazaunin Kaduna.

Design a site like this with WordPress.com
Get started